News
Trending

Mutum 1M na Barazanar fara zanga-zanga kan cigaba da rike el-rufa’i

Matasa na barazanar fara tattakin mutum miliyan 1 a Abuja kan ci gaba da tsare El-rufai

Zanga-zanga ta ɓarke a wasu sassan Jihar Kaduna kan ci gaba da tsare tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, inda matasa suka nemi a sake shi nan take.

Masu zanga-zangar sun ce tsare shi duk da shari’ar da ke gaban kotu na tayar da tambayoyi kan bin doka, tare da barazanar shirya tattakin mutum miliyan ɗaya a Abuja idan ba a sake shi ba.

Wasu ‘yan adawa sun danganta lamarin da abin da suka kira takura wa muryoyin adawa, suna mai cewa har da kama tsohon AGF, Abubakar Malami.

Zanga-zangar ta zo ne yayin da jami’an DSS suka gaza gabatar da shi a kotu kan zargin laifukan yanar gizo.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito an gudanar da zanga-zangar a Kaduna da Kafanchan cikin lumana, ba tare da rahoton tashin hankali ba.

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button