
A ƴan kwanakin nan sojojin Najeriya sun bayyana samun nasara a yaƙin da suke yi da ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP a jihar Borno.
Ko a ranar Lahadi, sojojin sun bayyana kisan Abu Khalid, “mutum na biyu mafi girman muƙami a Boko Haram a yankin dajin Sambisa,” a cewar sanarwar da sojojin suka fitar.
Sanarwar ta ce sun samu nasarar kashe Abu Khalid, da wasu mayaƙansa 10 a wani samame cikin dare da suka kai maɓoyar mayaƙan.
Kisan nasa na zuwa ne kwana daya bayan sojoji sun kawar da wani gawurtacen kwamandan Boko Haram, da ake kira Julaibib a yankin Gujba.




